Wannan Littafi Manufarsa shine ya baiwa Musulmi karfin gwiywa wajen Tabbatar da Zuwan Annabi Isa (as) da Hazrat Mahdi (as) kuma ya kyautu ga duk wanda yake da Sha’awa gameda sanin Zuwansu Annabi Isa (as) da Mahdi, Ya samu ingantaccen ilmi ta hanyoyin suka dace daga Sahihan Hadisai wanda aka samo daga Manyan Littafai masu Nagarta daga Annabi (SAW) da kuma Littatafai masu Tsarki da Daraja, Wanda ake amfani dasu tun daga Zamanin Annabawa har zuwa Wannan Zamani da muke ciki.Ta irin Wannan Ilmi ne Addinin Musulunci, Musulmi da duk Wanda yake Rayuwa a Bayan Kasa, Zasuyi Biyayya ga Zuwan Wadannan Mashahuran Bayin Allah Guda Biyu da Abubuwan da Zasu auku lokacin Bayyanar su, Kuma zaisa a dauki Wannan Al’amari na Zuwan su da Muhimmanci tare da Bayyana Murna da Farin ciki Wajen Samun Cigaban Addinin Musulunci a Wannan Lokaci, Kuma Zai Baiwa Musulmi Daman su Shiryawa wa Wannan Babban Al'amari Dazai faru na Tarihi nan gaba.
2010-07-09 14:03:16